Gombe Reporters

Gombe Reporters

Share

Sahihan Labaru Da Dumi Duminsu

Photos from Gombe Reporters's post 06/07/2026

Rikicin Manoma da Makiyaya a Daban Fulani, Jihar Gombe

Mazauna garin Daban Fulani da ke Ƙaramar Hukumar Kwami a Jihar Gombe sun yi kira ga gwamnati da jami'an tsaro da su gaggauta ɗaukar mataki kan yawaitar rikicin manoma da makiyaya a yankin.

Wasu daga cikin waɗanda s**a jikkata sun ce shanun makiyaya sun lalata amfanin gonakinsu da kayan noma na miliyoyin naira. Sun kuma zargi cewa an kai musu hari yayin da suke ƙoƙarin hana dabbobin shiga gonakinsu.

Sun buƙaci a hukunta masu hannu a rikicin tare da ɗaukar matakan tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al'umma. A lokacin haɗa wannan rahoto, ba a samu jin ta bakin makiyayan kan zarge-zargen ba.

Want your business to be the top-listed Media Company in Gombe?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Address

Beside Bima Lodge Gombe, Gombe Stat
Gombe