Yunusa Rabiu Tahir
Allah yasa aljanna makomarmu
19/08/2025
WALE EDUN, DAKE SHUGABANTAR KUNGIYAR SHIRIN TATTALIN ARZIKIN NAJERIYA, YA GANA DA GWAMNAN BABBAN BANKIN NAJERIYA DON KARFAFA HADIN GWIWAR TSARE-TSAREN KUDI DANA KASAFI
Mai Girma Ministan Kudi da kula da tattalin arzikin ƙasa, Mista Wale Edun, wanda shi ne kuma shugaban Ƙungiyar Shirye-shiryen Tattalin Arzikin Ƙasa, a yau ya gudanar da muhimmin taro tare da Gwamnan Babban Bankin Najeriya (CBN), Dakta Olayemi Cardoso, a Hedikwatar CBN dake Abuja. Shugaban Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS), Dakta Zacch Adedeji, shi ma ya halarci taron.
Wannan tattaunawar ta matakin koli ta nuna muhimmancin daidaita manufofin kudi da na kasafi a ƙarƙashin jagorancin Edun domin tabbatar da zaman lafiyar tattalin arziki, ƙarfafa gwiwar masu zuba jari, da kuma hanzarta cigaban dake karkashin jagorancin masu zaman kansu.
Mista Edun ya jaddada cewa, hadin kai tsakanin hukumomin kula da kudade dana kasafin kudi nada matuƙar muhimmanci wajen aiwatar da shirin gyaran tattalin arzikin Shugaba Bola Tinubu, wanda ke tabbatar da cewa an takaita hauhawar farashi, an tara kudaden shiga yadda ya kamata, kuma rancen kudi yana tafiya yadda ya dace zuwa sassan tattalin arzikin dake samar da aiki daci gaba.
“Kwakwanso will not join the APC unless Tinubu resolves the Emirate issue in Kano… Inji Buba Galadima
Salon da s**ayi lokacin shari'ar zabe 😂😂
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Website
Address
Kano Outlying