IMACS TV
IMAMU AHMAD CENTER FOR STUDIES TV
26/02/2026
Lokutan buɗa baki da sahur a jihar Kano.
Daga IMACS TV/RADIO 📻
26/02/2026
Da Dumi-Dumi
DSS sun saki Walida
Gwamnan jihar Jigawa, Umar Namadi, ya karbi Walida Abdulhadi Ibrahim, yarinyar da aka ce ta bace daga jihar, wadda ta kasance a hannun jami’an DSS.
Gwamnan ya bayyana cewa dukkan batutuwan da s**a shafi zargin sace ta za su bi hanyar doka, yana mai jaddada cewa kotuna ne za su yanke hukunci kan lamarin.
Ya kuma ba da tabbacin cewa za a tabbatar da adalci, tare da tabbatar wa jama’a cewa gwamnati za ta bar doka ta yi aikinta yadda ya kamata.
26/02/2026
YANZU YANZU | Kamfanin Jiragen Sama na Saudiyya SaudiAirlines zai sake fara zirga-zirga daga Jeddah zuwa Abuja a watan Yuni, ko kuma zuwa watan Janairu na shekarar 2027".
Jakadan Saudiyya a Najeriya Ambasada Yousef Bin Muhammed Al-Balawi, ya bayyana hakan ne a ranar Laraba yayin wata ziyarar girmamawa da ya kai wa Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Mohammed Idris, a ranar Laraba, a ofishinsa da ke Abuja.
Ya ce dawowar wannan zirga-zirgar jiragen sama za ta ƙara sauƙaƙa tafiye-tafiye tsakanin Najeriya da Saudiyya, tare da ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu.
📷 Ma'aikatar yada labarai.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the business
Telephone
Website
Address
Kano
IMAMUAHMADCENTERFORSTUDIES6