Lakechad Reporters
Realistic Sources of Informations of LakeChad Area And Other Parts Of The World.
10/02/2023
Sauyin kuɗi: Ganduje ya maka Buhari a Kotun Ƙoli
Gwamnatin Jihar Kano, ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ta maka gwamnatin tarayya a gaban Kotun Ƙoli kan matakin da babban bankin Najeriya ya dauka na dakatar da amfani da tsofaffin kudaden naira.
A wata kara da babban Lauyan jihar Kano kuma kwamishinan shari’a, Musa Lawan ya shigar a jiya Alhamis, gwamnatin Kano ta kuma bukaci kotun ta dakatar da manufar babban bankin Najeriya na fitar da kudade har sai an yanke hukunci. harka.
A cewar takardun kotun an shigar da babban lauyan gwamnatin tarayya, Abubakar Malami a matsayin wanda ake kara a gaban kotu.
Gwamnatin Kano ta bukaci a fassara sashe na 148 (2), Sashe na 1, sakin layi na 19 zuwa Jadawali na uku na Kundin Tsarin Mulkin Tarayyar Najeriya (1999) da Sashe na 19 da 20 na Dokar Babban Bankin Najeriya ta 2007.
Gwamnatin Kano ta kuma bukaci kotun koli da ta bayar da umurnin cewa: “Hukunci na gaggawa na wannan kotun mai girma da ta haramtawa gwamnatin tarayyar Najeriya ita kanta, jami’anta, ma’aikatanta, wakilanta, masu zaman kansu, ‘yan amshin shata ko wakilai da sunan ko aka kira, musamman Babban bankin Najeriya, bankunan kasuwanci, kamfanoni, ma'aikatu, kwamitoci, hukumomi, ma'aikatu, ko duk wata hukuma ko wacce doka ta sani ko doka ta kafa daga dakatar da ko dakatar da amfani da tsoffin takardun kuɗi na N200 (Naira Dari Biyu). ), Naira 500 (Naira Dari Biyar) da N1000 (Naira Dubu Daya) a daga ranar 10 ga Fabrairu, 2023, har sai an jira ranar sauraron karar da mai gabatar da kara/Mai kara akan Sanarwa kan wannan lamari,"
Haka zalika gwamnatin ta nuna cewa Buhari bashi da ikon da zai baiwa CBN umarnin daina amfani da kuɗaɗen N200, N500 da N1000 ba.
20/01/2023
The way Lionel Messi looks at Cristiano Ronaldo 🥰
18/01/2023
Kyari Bawuro Da Amaryar sa, Allah Ya Bada Zaman Lafiya
16/01/2023
This is Gombe, the capital city of Gombe state, Nigeria 🇳🇬. Also known as; the Jewel In The Savannah.
Credit: Northeast Reporters
09/01/2023
Matar Daraktan SSS ta sa an tsare Abba Gida-gida tare da barazanar kashe hadiminsa a filin jirgin sama a Kano
Mai ɗakin Darakta-Janar na hukumar jami'an tsaro na farin kaya, SSS, Aisha Yusuf Bichi, ta bada umarnin a tsare ɗan takarar gwamna na jam'iyyar NNPP a Kano, Abba Kabir Yusuf, inda ta hana shi hawa jirgi da ga Kano zuwa Abuja.
DAILY NIGERIAN ta jiyo cewa dambarwar ta faru ne a kofar shiga ɓangaren matafiya masu alfarma na filin jirgin saman Malam Aminu Kano, yayin da ayarin motocin Yusuf, wanda a ka fi sani da Abba Gida-gida, su ka haifar da cinkoso.
Lamarin ya haifar wa da ayarin motar Aisha Bichi tsaiko, yayin da ta ke shiga ɓangaren domin tashi zuwa Abuja.
Majiyoyi sun shaida wa DAILY NIGERIAN cewa lamarin ya fusata Aisha Bichi, inda dogaranta su ka riƙa duka kan mai uwa da wabi da ababen hawa saboda "raina Hajiya".
Shaidun gani da ido sun ce da ƙurar ta lafa, sai Abba Gida-gida ya je don ya yi mata ƙorafin abinda dogaranta su ka yi, a matsayin ta na ƙawar mai ɗakin sa, inda ta riƙa yi masa balbalin-bala'i, har ta ke cewa ba za ta bari ya yi gwamna a Kano ba.
Daga nan dai, in ji majiyoyi, sai ga ƙarin jami'an tsaron farin kaya sun zo, inda su ka tsare Abba Gida-gida har sai da Aisha Bichi ta shiga jirgi ta tashi zuwa Abuja.
Wasu majiyoyin ma sun ce kafin ta tashi zuwa Abuja, a lokacin da ta ke ta faɗa, Aisha Bichi ta hango wani hadimin Abba Gida-gida, Garba Kilo yana ɗaukar ta a waya, inda ta sa dogaran ta su "harbe shi kuma ba abin da za a yi."
"Ta ci gaba da faɗa, ta kuma rantse cewa Abba Gida-gida ba zai shiga jirgi ɗaya da ita ba. Haka dai aka ci gaba da tsare Abba har sai da jirgin ya tashi matar Daraktan," in ji majiyar.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the business
Website
Address
Maiduguri