AMANA PRESS

AMANA PRESS

Share

An samar da wannan kafar ce domin bayar da labarai kamar yadda suke ba tare da nuna wani bambanci ko son rai ba. Haka ma muna fassara wato Translation.

Photos from AMANA PRESS's post 05/04/2026

RAHOTO: Zuwan Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan Zuwa Jam’iyyar ADC

Daga: Faruq Sani Kudan

An gudanar da wani gagarumin taro a yau inda tsohon ɗan takarar gwamna a Jihar Kaduna, Hon. Isa Ashiru Kudan, ya sanar da sauya sheƙa tare da shiga sabuwar jam’iyyar siyasa ta ADC (African Democratic Congress).

A cikin jawabin nasa, Hon. Isa Ashiru Kudan ya jaddada muhimmancin wayar da kan al’umma, inda ya ce lokaci ya yi da jama’a za su farka daga halin da suke ciki, su nemi mafita mai dorewa domin samun ingantacciyar shugabanci a zaɓe mai zuwa na shekarar 2027.

“Al’umma ya kamata su farka sosai, su duba halin da ake ciki, su kuma nemi mafita da za ta kai su ga makoma mai kyau,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa akwai mutane da dama a Jihar Kaduna da s**a fara komawa jam’iyyar ADC, yana mai cewa wannan alama ce da ke nuna yadda jama’a ke neman sauyi a harkar siyasa.

Haka zalika, ya yi kira ga al’umma da kada su bari a rinjaye su da kuɗi yayin zaɓe. Ya ce:

“Idan s**a ba ku kuɗi, ku karɓa, amma ku tabbatar kun yi zaɓin da ya dace da zuciyarku a wajen kaɗa ƙuri’a a zaɓen 2027.” ku kada su su faɗi ƙasa warwars

Hon. Isa Ashiru Kudan ya ƙara da cewa jam’iyyar ADC na da burin kawo sauyi na gaskiya tare da samar da shugabanci nagari wanda zai inganta rayuwar al’umma baki ɗaya.

Rahotanni sun nuna cewa wannan sauya sheƙa na iya sauya yanayin siyasa a Jihar Kaduna, musamman ganin yadda magoya baya ke ci gaba da sauya akala zuwa sabuwar jam’iyyar.

30/03/2026

Idan baka mutu ba komai sai ka gani a wannan duniya .

12/03/2026

Yanzu shi ke nan babu 'yan adawa a Nijeriya?

11/03/2026

Abubuwan da ake buƙata aikatawa kwana goma na karshen Ramadan tare da Zainab Idris Bamalli (Kilishin Barden Malaman Zazzau)

09/03/2026

Kwalejin Tulip International Kaduna ta shirya wa 'Yan Jarida bukin shan ruwa

09/03/2026

Abin da ya kamata ku aikata a goman karshe na watan Ramadan

Want your business to be the top-listed Media Company in Kaduna?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Address


Kaduna