Ibrahim Abdullahi
I'm a membar at kannywood
C O E OF FIKIRA MULTIMEDIA
DIRECTOR
PRODUCER
BUSINESS MAN
TEACHER JASS
Innalillahi wa innailaihir rajuon Allah ya yi wa Baba rasuwa! đĽ˛
Allah kara lfy Baba Ado
ubangiji yakiyaye gaba
22/05/2025
Yadda na roĆi YarâAdua kada ya yi fada da Obasanjo â Sule Lamido
Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya bayyana yadda ya roĆi marigayi Shugaba Umaru Musa YarâAdua kada ya shiga rikici da tsohon Shugaban Ćasa Olusegun Obasanjo.
A shafuka na 257 da 258 na tarihin rayuwarsa da ya rubuta mai suna âBeing True To Myselfâ, wanda aka gabatar wa jamaâa a ranar 13 ga Mayu, 2025, Lamido ya bayyana wasu abubuwa biyu da s**a ba shi tabbacin cewa akwai rikici tsakanin YarâAdua da Obasanjo.
Batun Naira biliyan $16 na NIPP
Lamido ya ce ya fara zargin hakan ne lokacin da aka fara tattaunawa a Majalisar Wakilai kan shirin samar da wutar lantarki na National Integrated Power Project (NIPP) da aka kashe fiye da dala biliyan $16.
Ya ce:
> âIdan dan adawa ne ya jagoranci wannan muhawara a Majalisar, hakan zai iya zama da sauki. Amma abin mamaki shi ne, wani babban Éan jamâiyyar PDP daga Jihar Katsina kuma aminin Shugaba YarâAdua ne ya jagoranci lamarin.
âAna ba da hoton cewa Obasanjo ne ya wawuri kuÉin, kuma an bar ayyukan a cikin daji. Duk da haka, daga baya abubuwa sun sha bamban.â
Lamido ya ce ya garzaya wajen Shugaba YarâAdua domin sanar da shi, amma YarâAdua ya ce:
> ââWannan batu ne da wata madasar gwamnati mai cin gashin kanta ke tattaunawa kai.ââ
Kirar daga CSO Tilde
Lamido ya ce abin da ya fi daukar hankalinsa shi ne lokacin da Tilde, jamiâin tsaro na fadar shugaban kasa (CSO), ya kira shi a lokacin yana ofis a Dutse.
> âDa na Éaga waya, sai Tilde ya tambaye ni ina nake, na ce masa kawai, âIna babban garina Dutseâ.
âAmma abin mamaki sai ya ce, âNa yi zaton kana Ota tare da shugaban kaâ â sai na saki baki. Bayan na dawo hayyacina, sai na zazzaga masa zagi iri-iri, na kuma ce zan kai kara wurin Shugaban Ćasa.
âDon lallashi sai ya ce, âDon Allah ku gafarce ni, na kira ne kawai don in shaida maka cewa an aiko da koke a kanka zuwa ga Shugaban Ćasa, kuma ina da ikon dakatar da binciken.ââ
Lamido ya ce bai sauko ba, sai ya ce masa:
> âWa kake tsammanin zaka yi wa barazana? Je ka lahira!â
Ganawa da YarâAdua a Villa
Bayan haka, Lamido ya ce ya Éauki jirgi ya wuce kai tsaye fadar shugaban Ćasa. Ya shiga ofishin Tilde, ya kuma zazzaga masa zagi a gaban kowa.
Daga nan ya hau sama ya shiga ofishin Shugaba YarâAdua.
YarâAdua ya tambaye shi:
> ââSule, me ke damunka haka?ââ
Lamido ya ce cikin rudani da fargaba, ya kusa durĆusawa, yana cewa:
> ââDon Allah, kada ka yi fada da Obasanjo. Kai mutum ne mai asali da daraja daga gida mai mutunci. A cikin addininmu da alâadunmu, bai dace mu nuna halin rashin godiya ba ga wanda ya tsaya mana a lokacin bukata. Obasanjo ne ya tsaya maka har ka zama Shugaban Ćasa.ââ
YarâAdua ya ce masa:
> ââSule, ka zauna ka nutsu.ââ Sai ya kira ADC Éinsa, Laftanar Kanal Mustapha.
YarâAdua ya tambayi ADC Éin:
> ââMenene umarnina game da Obasanjo?ââ
ADC Éin ya ce:
ââKa ce in amince da duk wani bukatarsa, ko a cikin gida ko wajen Ćasa, ba tare da sai an nemi amincewarka ba.ââ
Daga nan YarâAdua ya ce masa:
> ââSule, yanzu ka huta?ââ
Lamido ya ce:
ââNa huta, Ranka ya dade,ââ sannan ya yi sallama ya tafi.
02/09/2024
With mama hajjo
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Contact the public figure
Telephone
Website
Address
Kano