Kokiya

Kokiya

Share

Jaridar Kokiya jarida ce Mai yada labarai cikin harshen Hausa

domin Karin bayani +2348068171406

09/06/2026

Tunda bayan da Tijjani Gandu yayi waƙar Hayaniyan bana, tiri tirin bana, Matsaltsalun bana, banda mu, Har yau Kwankwasawa cikin matsala suke.

Ba su sake samun zaman nitsuwa ta watanni Uku masu kyau a jam'iyya ɗaya ba.

NNPP - Matsaltsalun Bana

ADC - Tiri - Tirin Bana

NDC - Hayaniyar Bana

Yanzu kuma ana tunanin cewar za su abka cikin Cakwalkalin cakwakiyar bana.

Daga Haj Shehu

08/06/2026

'Yan Bindiga Sunyi Garkuwa da Dattawan Zamfara, 50 Bayan da Sukaje Neman Sulhu:

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da dattawa 50 da daga kauyen Magamin Diddi da ke yankin Magami/Faru a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara, yayin da s**aje yin sulhu da wani shugaban ‘yan bindiga da ake kira Jammo.

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban ‘yan bindigar ne ya nemi a yi sulhu, bayan wasu daga cikin mutanensa sun mutu a wani sumame da jami’an tsaro s**a kai.

Sai dai bayan da kwamitin mutum 50 da al’ummar yankin s**a tura ya isa wurin ganawar, sai ‘yan bindigar s**a yi garkuwa da su.

Shugaban karamar hukumar Maradun, Bello Dosara ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce dattawan sun shirya yin sulhun ne ba tare da amincewa ko sanin gwamnatin jihar ba.

Ya kara da cewa gwamnatin jihar Zamfara ba ta goyon bayan yin sulhu da ‘yan bindiga.

08/06/2026

Iran ta harba "kusan mak**ai masu linzami 30" kan Isra'ila tun a daren Lahadin da ya gabata, in ji wani jami'in sojan Isra'ila da sanyin safiyar Litinin ɗin nan.

08/06/2026

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta karɓi wata ƙara da ke neman a soke rajistar Jam'iyyar NDC tare da cire ta daga cikin jerin jam'iyyun siyasa masu rajista a Najeriya.

Siyasarmu TV ta rawaito a rahoton Daily Trust cewa an shigar da ƙarar ne a ranar Talatar makon da ya gabata ƙarƙashin lamba FHC/ABJ/CS/1115/2026, kuma an miƙa shari'ar ga Mai Shari'a Mohammed Umar bayan Babban Alƙalin Kotun Tarayya, Mai Shari'a John Tsoho, ya yi rabon shari'ar.

Masu shigar da ƙarar suna neman kotun ta binciki sahihancin rajistar jam'iyyar tare da ɗaukar matakin da ya dace kan ci gaba da kasancewarta a matsayin jam'iyyar siyasa mai rajista.

Sai dai wanda ya assasa jam'iyyar kuma jagoranta na ƙasa, Seriake Dickson, ya bayyana cewa babu wata ƙara ko ɗaukaka ƙara da ke gaban kotu da ke ƙalubalantar rajistar NDC, yana mai jaddada cewa jam'iyyar tana aiki bisa tanadin doka.

07/06/2026

'Yansanda cun ceto ƴar uwar tsohon ministan wutar lantarki da tagwayen ta da aka sace a Ibadan

Rundunar 'yansandan Najeriya ta tabbatar da ceto Misis Busayo Adelabu-John Paul da 'ya'yanta tagwaye masu shekara 12, Peter da Paul, bayan da wasu masu garkuwa da mutane s**a sace su a ranar 3 ga watan Yuni a birnin Ibadan na Jihar Oyo.

Mai magana da yawun rundunar, DCP Anthony Placid, ya bayyana a wata sanarwa ranar Lahadi cewa jami'an sashen tattara bayanan sirri na rundunar (FID-IRT) sun gudanar da wani samame na musamman a Ibadan da misalin karfe 7:30 na yammacin ranar Asabar, inda s**a yi nasarar kubutar da mutanen ba tare da sun ji rauni ba.

A cewarsa, nasarar ta samu ne bayan tattara bayanan sirri, sa ido da kuma dabarun aiki da s**a bai wa jami'an damar gano motsin masu garkuwar. Hakan ya kai ga artabu tsakanin jami'an tsaro da wadanda ake zargi.

Placid ya ce an harbe mutum biyu daga cikin wadanda ake zargin har s**a mutu, yayin da aka kwato bindigogi biyu. Ya kara da cewa an kai wadanda aka ceto wurin da ya dace domin samun kulawar lafiya da sauran tallafi.

Babban Sufeton 'Yan Sandan Najeriya, Tunji Disu, ya yaba da jajircewa da kwarewar jami'an da s**a gudanar da aikin, yana mai cewa kokarinsu ne ya tabbatar da kubutar da mutanen cikin koshin lafiya.

Rundunar ta kuma bayyana cewa ana ci gaba da farautar sauran mambobin kungiyar masu garkuwar da s**a tsere, inda bayanan farko s**a nuna cewa wasu daga cikinsu sun tsere da raunukan harbin bindiga.

An sace Misis Busayo Adelabu-John Paul, wadda ke kanwar tsohon Ministan Wutar Lantarki, tare da 'ya'yanta tagwaye a safiyar ranar 3 ga Yuni yayin da take kai su makaranta a yankin Elewura da ke Challenge a Ibadan. Lamarin ya jawo damuwa a tsakanin iyalanta da kuma al'ummar siyasar Jihar Oyo.

06/06/2026

Gwanin Burgewa: Yadda shugaban ƙaramar hukumar Mafara dake jihar Zamfara, Hon. Yahaya Yari, ya haye saman dutse a cikin daji inda 'yan bindiga ke yawo tare da bayyana cewa ya shirya mutuwa akan al'ummarsa da yake shugabanta,

Mezakuce?

Want your public figure to be the top-listed Public Figure in Kano?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Category

Website

Address


Kano