Ayzan Multimedia
Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Ayzan Multimedia, Broadcasting & media production company, Kano.
17/02/2026
🕌 DA DUMI-DUMI 🕌
An tabbatar da ganin jinjirin watan Ramadan 1447H a Saudi Arabia.
Hukumar kula da harkokin shari’a da ganin wata ta sanar da cewa, za a fara azumin watan Ramadan daga daren yau, wanda ya yi daidai da shekarar 2026 Miladiyya.
Ramadan wata ne na rahama, gafara da kubuta daga wuta. Wata ne da Al-Qur’ani ya sauka, kuma lokaci ne na ƙara kusanci da Allah ta hanyar azumi, sallah (Qiyamul-Layl), sadaqa da sauran ibadu.
Muna roƙon Allah ﷻ Ya karɓi azuminmu, tsayuwar darenmu da addu’o’inmu, Ya sa mu dace da cin moriyar wannan wata mai albarka
12/02/2026
Jami’an tsaro sun kwace fasfon El-Rufai bayan yunkurin k**a shi ya ci tura – Muyiwa
An yi yunkurin k**a tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a ranar Alhamis.
Mai ba shi shawara kan harkokin yada labarai, Muyiwa Adekeye, ne ya bayyana hakan ta cikin jerin sakonni da bidiyo da ya wallafa a shafukan sada zumunta.
Ya ce El-Rufai na dawowa ne daga birnin Cairo na kasar Masar lokacin da jami’an tsaro s**a tare shi.
Adekeye ya ce jami’an sun nufi tsohon gwamnan ne da zarar ya sauka daga jirginsa, inda s**a nemi su tafi da shi domin tsare shi.
A cewarsa, tsohon gwamnan ya ki bin su, yana mai jaddada cewa ba zai amince da bukatar ba sai an gabatar masa da gayyata ta hukuma.
Sakon ya ce: “Jami’an tsaro a yau sun yi yunkurin k**a Malam Nasir El-Rufai yayin da ya iso daga Cairo. Malam El-Rufai ya ki bin su ba tare da gayyata ta hukuma ba.”
Adekeye ya kuma yi zargin cewa jami’an tsaron sun kwace fasfon tsohon gwamnan yayin da lamarin ke faruwa.
“Duk da haka, sun kwace fasfonsa daga hannun wani mataimaki,” in ji shi.
Click here to claim your Sponsored Listing.
Category
Telephone
Address
Kano