Blueprint Hausa

Blueprint Hausa

Share

Contact information, map and directions, contact form, opening hours, services, ratings, photos, videos and announcements from Blueprint Hausa, Media/News Company, Katsina.

26/02/2026

Da Ɗumi-Ɗumi:- Dole Ne Nasiru Elrufa'i Ya Fuskanci Hukunci - Inji Kungiyoyin matasan Arewacin Najeriya

Ƙungiyoyin fararen hula daga Arewacin Najeriya da kuma kudancin kasar nan sun jaddada kiran cewa dole Elrufa'i ya fuskanci dukkan tuhume-tuhumen da ake masa, babu wani tsohon shugaba da yafi karfin doka ko waye shi.

Abubuwan daya aikata lokacin da yake kan karagar mulki tun daga kwace kadarorin al'umma, take hakkin dan'adam, k**a mutane ba gaira ba dalili, ya zama dole yanzu ya fuskanci hukuncin abinda ya aikata.

Daga Nura Jamilu
Shugaban masu rajin kare demokradiyya na Kaduna

14/02/2026

Ba Ribadu Ne Matsalarka Ba: Gwamnatin Jihar Kaduna Ce Ta Kai Ka Gaban Hukuma Ka Tafi Ka Amsa Laifukan Da Ake Tuhumarka

Ya k**ata ka Fuskanci Zarge-Zargenka, Ka Daina Ɗorawa Wasu Laifi.

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, dole ne ya daina yaudarar jama’a ta hanyar karkatar da akala daga ainihin batun da ake tuhumarsa da shi.

Zarge-zargen cin hanci da rashawa da almundahana da s**a taso daga mulkinsa ba ƙananan batutuwa ba ne da za a shafe su da siyasa ko surutai.

Abin da ya fi ba jama’a mamaki shi ne yadda yake ƙoƙarin janyo sunan Nuhu Ribadu cikin wannan rikici, alhali ba shi ne ya kai ƙarar ba. Gwamnatin Jihar Kaduna ce da kanta ta miƙa batun ga Independent Corrupt Practices Commission (ICPC) da kuma Economic and Financial Crimes Commission (EFCC) domin a bincike shi.

Don haka duk wani yunƙuri na jefa wani cikin wannan batu wata dabara ce ta neman kawar da hankali daga gaskiya.
A lokacin mulkinsa a Kaduna State, an sha fama da zarge-zargen karkatar da kuɗaɗen jama’a, rushe gidaje ba tare da adalci ba, da yanke shawara ba tare da bin ƙa’ida ba.

Yanzu da aka buɗe bincike, abin da ya k**ata shi ne ya fito ya kare kansa a gaban doka, ba ya ɓoye a bayan siyasa ba.
Idan yana da gaskiya, kotu da hukumomin yaƙi da cin hanci za su tabbatar. Amma idan akwai laifi, dole ne ya fuskanci hukunci k**ar kowane ɗan ƙasa.

Bayan zarge-zargen cin hanci da rashawa, Elrufa'i ya kasance mutum mafi take hakkin mutane a lokacin da yake mukin jihar Kaduna, cikin waɗanda ya gallazawa har da su tsohon sanatan Kaduna ta tsakiya Sanata Shehu Sani.

Irin wannan mutanen ba su cancanci tausayawa agun talakawa ba ko kaɗan, Yak**ata su fuskanci hukunci mai tsauri akan abubuwan da s**a aikata.

Daga matashin Ɗan gwagwarmaya
Muhammad Nur Kaduna.

Want your business to be the top-listed Media Company in Katsina?
Click here to claim your Sponsored Listing.

Telephone

Address


Katsina